< Zabura 132 >

1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
Un cántico de los peregrinos que van a Jerusalén. Señor, acuérdate de David, y todo por lo que él pasó.
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
Él hizo una promesa al Señor, un pacto al Dios de Jacob:
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
“No iré a casa, no iré a la cama,
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
no me iré a dormir, ni tomaré una siesta,
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
hasta que haya encontrado un lugar donde el Señor pueda vivir, un hogar para el Dios de Jacob”.
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
En Efrata, oímos hablar del arca del pacto, y la encontramos en los campos de Yagar.
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
Vayamos al lugar donde mora el Señor y postrémonos ante sus pies en adoración.
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
Ven, Señor, y entra a tu casa, tú y tu arca poderosa.
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
Que tus sacerdotes se revistan de bondad; que los que te son leales griten de alegría.
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
Por el bien David, tu siervo, no le des a la espalda a tu ungido.
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
El Señor le hizo una promesa solemne a David, una que él una rompería, “pondré a uno de tus descendientes en tu trono.
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
Si tus hijos siguen mis leyes y los acuerdos que les enseñe, también sus descendientes se sentarán en el trono para siempre”.
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
Porque el Señor ha escogido a Sión, y quiso hacer su trono allí, diciendo:
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
“Esta siempre será mi casa; aquí es donde he de morar.
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
Proveeré a las personas de la ciudad todo lo que necesiten; alimentaré al pobre.
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
Revestiré a sus sacerdotes con salvación; y los que le son leales gritarán de alegría.
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
Haré el linaje de David aún más poderoso. He preparado una lámpara para mi ungido.
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
Humillaré a sus enemigos, pero las coronas que él use brillarán fuertemente”.

< Zabura 132 >