< Zabura 132 >

1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
Песнь восхождения. Вспомни, Господи, Давида и все сокрушение его:
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
как он клялся Господу, давал обет Сильному Иакова:
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
“не войду в шатер дома моего, не взойду на ложе мое;
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
не дам сна очам моим и веждам моим - дремания,
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
доколе не найду места Господу, жилища - Сильному Иакова”.
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
Вот, мы слышали о нем в Ефрафе, нашли его на полях Иарима.
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
Пойдем к жилищу Его, поклонимся подножию ног Его.
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
Стань, Господи, на место покоя Твоего, - Ты и ковчег могущества Твоего.
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
Священники Твои облекутся правдою, и святые Твои возрадуются.
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
Ради Давида, раба Твоего, не отврати лица помазанника Твоего.
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
Клялся Господь Давиду в истине, и не отречется ее: “от плода чрева твоего посажу на престоле твоем.
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
Если сыновья твои будут сохранять завет Мой и откровения Мои, которым Я научу их, то и их сыновья во веки будут сидеть на престоле твоем”.
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
Ибо избрал Господь Сион, возжелал его в жилище Себе.
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
“Это покой Мой на веки: здесь вселюсь, ибо Я возжелал его.
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
Пищу его благословляя благословлю, нищих его насыщу хлебом;
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
священников его облеку во спасение, и святые его радостью возрадуются.
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
Там возращу рог Давиду, поставлю светильник помазаннику Моему.
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
Врагов его облеку стыдом, а на нем будет сиять венец его”.

< Zabura 132 >