< Zabura 132 >
1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
canticum graduum memento Domine David et omnis mansuetudinis eius
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
sicut iuravit Domino votum vovit Deo Iacob
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
si introiero in tabernaculum domus meae si ascendero in lectum strati mei
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
si dedero somnum oculis meis et palpebris meis dormitationem
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
et requiem temporibus meis donec inveniam locum Domino tabernaculum Deo Iacob
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
ecce audivimus eam in Efrata invenimus eam in campis silvae
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
introibimus in tabernacula eius adorabimus in loco ubi steterunt pedes eius
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
surge Domine in requiem tuam tu et arca sanctificationis tuae
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
sacerdotes tui induentur iustitia et sancti tui exultabunt
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
propter David servum tuum non avertas faciem christi tui
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
iuravit Dominus David veritatem et non frustrabit eum de fructu ventris tui ponam super sedem tuam
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
si custodierint filii tui testamentum meum et testimonia mea haec quae docebo eos et filii eorum usque in saeculum sedebunt super sedem tuam
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
quoniam elegit Dominus Sion elegit eam in habitationem sibi
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
haec requies mea in saeculum saeculi hic habitabo quoniam elegi eam
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
viduam eius benedicens benedicam pauperes eius saturabo panibus
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
sacerdotes eius induam salutari et sancti eius exultatione exultabunt
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
illic producam cornu David paravi lucernam christo meo
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
inimicos eius induam confusione super ipsum autem efflorebit sanctificatio mea