< Zabura 132 >

1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
(성전에 올라가는 노래) 여호와여, 다윗을 위하여 그의 모든 근심한 것을 기억하소서
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
저가 여호와께 맹세하며 야곱의 전능자에게 서원하기를
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
내가 실로 나의 거하는 장막에 들어가지 아니하며 내 침상에 오르지 아니하며
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
내 눈으로 잠들게 아니하며 내 눈꺼풀로 졸게 아니하기를
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
여호와의 처소 곧 야곱의 전능자의 성막을 발견하기까지 하리라 하였나이다
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
우리가 그것이 에브라다에 있다 함을 들었더니 나무 밭에서 찾았도다
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
우리가 그의 성막에 들어가서 그 발등상 앞에서 경배하리로다
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
여호와여, 일어나사 주의 권능의 궤와 함께 평안한 곳으로 들어가소서
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
주의 제사장들은 의를 입고 주의 성도들은 즐거이 외칠지어다
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
주의 종 다윗을 위하여 주의 기름 받은 자의 얼굴을 물리치지 마옵소서
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
여호와께서 다윗에게 성실히 맹세하셨으니 변치 아니하실지라 이르시기를 네 몸의 소생을 네 위에 둘지라
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
네 자손이 내 언약과 저희에게 교훈하는 내 증거를 지킬진대 저희 후손도 영원히 네 위에 앉으리라 하셨도다
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
여호와께서 시온을 택하시고 자기 거처를 삼고자 하여 이르시기를
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
이는 나의 영원히 쉴 곳이라 내가 여기 거할 것은 이를 원하였음이로다
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
내가 이 성의 식료품에 풍족히 복을 주고 양식으로 그 빈민을 만족케 하리로다
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
내가 그 제사장들에게 구원으로 입히리니 그 성도들은 즐거움으로 외치리로다
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
내가 거기서 다윗에게 뿔이 나게 할 것이라 내가 내 기름 부은 자를 위하여 등을 예비하였도다
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
내가 저의 원수에게는 수치로 입히고 저에게는 면류관이 빛나게 하리라 하셨도다

< Zabura 132 >