< Zabura 132 >
1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
Ein Stufenlied. - Sei, Herr, zugunsten Davids eingedenk all dessen, was er gesprochen,
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
wie er dem Herrn geschworen, dem Starken Jakobs hat gelobt:
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
"Ich gehe nimmer in mein Wohngezelt, besteige nicht mein Ruhebett,
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
Versage meinen Augen Schlaf und Schlummer meinen Augenwimpern,
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
bis daß ich eine Stätte finde für den Herrn, für Jakobs Starken eine Wohnung." -
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
Nun hörten wir davon zu Ephrat und fanden sie im Waldgefilde.
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
"Zu seiner Wohnung laßt uns gehen, vor seiner Füße Schemel niederfallen!"
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
Auf, Herr, zu Deiner Ruhestätte, Du und die Lade Deiner Herrscherwürde!
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
Mit Heil laß Deine Priester sich bekleiden, und Deine Frommen mögen jubeln! -
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
Um David, Deines Dieners willen, weis nicht zurück, den Du gesalbt!"
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
Der Herr schwur David Dauer zu. Er geht davon nicht ab. "Auf deinen Thron erheb ich einen von deiner Leibesfrucht.
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
Bewahren deine Söhne meinen Bund und meine Zeugnisse, wie ich sie lehre, dann dürfen ihre Söhne allezeit auf deinem Throne sitzen!" -
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
Der Herr hat Sion sich erkoren, zum Wohnsitz sich ersehen:
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
"Das sei in Ewigkeit mein Ruhesitz, ich throne hier; denn hier gefällt es mir.
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
Ich segne seine Jugend und gebe seinen Armen Brot in Fülle.
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
Mit Heil bekleid ich seine Priester, und frohe Lust sei seiner Frommen Teil!
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
Ich lasse Davids Macht ersprossen, dem richt ich eine Leuchte her, den ich gesalbt.
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
In Schande hüll ich seine Feinde, dieweil auf ihm ein Diadem erglänzt."