< Zabura 132 >

1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
Ein Stufenlied. / Gedenke, Jahwe, dem David / All die Opfer, die er gebracht.
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
Er leistete Jahwe einen Schwur, / Gelobte dem starken Gott Jakobs:
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
"Wahrlich, nicht geh ich ins Zelt meines Hauses, / Nicht besteig ich das Bett meines Lagers,
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
Nicht gönne ich Schlaf meinen Augen / Noch meinen Wimpern Schlummer:
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
Bis ich eine Stätte für Jahwe gefunden, / Eine Wohnung für Jakobs starken Gott."
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
Sieh, wir hörten, sie sei in Efrâta, / Wir haben sie dann in Jaars Gefilden gefunden.
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
So laßt uns denn in seine Wohnung gehn, / Uns niederwerfen vor seiner Füße Schemel.
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
Auf, Jahwe, begib dich zu deiner Ruhstatt, / Du und die Lade, das Bild deiner Macht!
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
Deine Priester werden dir dienen in Treue, / Und deine Frommen werden sich freun.
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
Um Davids, deines Knechtes, willen / Versage nicht deines Gesalbten Bitte!
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
Jahwe hat David geschworen / — Wahr ist's, nicht nimmt er's zurück —: / Von der Frucht deines Leibes / Will ich einen Mann auf den Thron dir setzen.
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
Halten deine Söhne den Bund mit mir / Und mein Zeugnis, das ich sie lehre: / So sollen auch ihre Söhne für immer / Dir auf dem Throne sitzen."
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
Denn Jahwe hat Zion erwählt, / Hat es zu seinem Wohnsitz begehrt:
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
"Dies ist meine Ruhstatt für immer; / Hier will ich bleiben, weil ich es begehrt.
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
Seine Nahrung will ich reichlich segnen, / Seine Armen sättigen mit Brot.
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
Seine Priester will ich kleiden in Heil, / Und seine Frommen sollen laut jauchzen.
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
Dort laß ich ein Horn für David sprossen: / Meinem Gesalbten hab ich eine Leuchte bereitet.
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
Seine Feinde will ich in Schande kleiden, / Aber auf ihm soll glänzen seine Krone."

< Zabura 132 >