< Zabura 132 >

1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
Cantique de Maaloth. Éternel, souviens-toi de David et de toute son affliction;
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
Lui qui jura à l'Éternel, et fit ce vœu au Puissant de Jacob:
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
Si j'entre sous l'abri de ma maison, et si je monte sur le lit où je repose;
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
Si je donne du sommeil à mes yeux, du repos à mes paupières;
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
Jusqu'à ce que j'aie trouvé un lieu pour l'Éternel, une demeure pour le Puissant de Jacob!
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
Voici, nous en avons entendu parler à Éphrath; nous l'avons trouvée dans les champs de Jaar.
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
Entrons dans ses demeures; prosternons-nous devant son marche-pied!
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
Lève-toi, ô Éternel, viens au lieu de ton repos, toi et l'arche de ta force!
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
Que tes sacrificateurs soient revêtus de justice, et que tes bien-aimés chantent de joie!
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
Pour l'amour de David, ton serviteur, ne rejette pas la face de ton Oint!
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
L'Éternel a juré la vérité à David, et il n'en reviendra pas: Je mettrai sur ton trône le fruit de tes entrailles.
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
Si tes fils gardent mon alliance et mes témoignages que je leur enseignerai, leurs fils aussi, à perpétuité, seront assis sur ton trône.
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
Car l'Éternel a fait choix de Sion; il l'a préférée pour y faire son séjour.
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
Elle est, dit-il, le lieu de mon repos, à perpétuité; j'y habiterai, car je l'ai choisie.
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
Je bénirai abondamment ses vivres; je rassasierai de pain ses pauvres.
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
Je revêtirai de salut ses sacrificateurs, et ses fidèles chanteront d'une grande joie.
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
C'est là que je ferai lever une corne à David, et que je prépare une lampe à mon Oint.
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
Je couvrirai de honte ses ennemis, et sur lui brillera son diadème.

< Zabura 132 >