< Zabura 132 >

1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
Cantique des degrés. Seigneur; souviens-toi de David et de toute sa mansuétude;
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
Comment il a juré au Seigneur et fait vœu au Dieu de Jacob.
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
Je n'entrerai pas, dit-il, dans le tabernacle de ma demeure; je ne monterai pas sur le lit de mon repos;
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
Je ne donnerai point de sommeil à mes yeux, ni à mes paupières le moindre assoupissement,
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
Ni de repos à mon front, avant que j'aie trouvé un lieu pour le Seigneur, un tabernacle pour le Dieu de Jacob.
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
Voilà que nous avons ouï dire: Il est en Éphrata; nous l'avons trouvé dans les plaines de la forêt.
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
Nous entrerons dans le tabernacle du Seigneur; nous l'adorerons dans le lieu où il a arrêté ses pieds.
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
Lève-toi, Seigneur, pour entrer en ton repos, toi et l'arche de ta sanctification.
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
Tes prêtres se revêtiront de justice, et tes saints seront transportés d'allégresse.
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
A cause de David ton serviteur, ne détourne pas ta face de ton Christ.
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
Le Seigneur a fait à David un serment véritable, et il ne le rétractera pas: Je placerai sur ton trône un roi issu du fruit de ton sang.
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
Si tes fils gardent mon alliance et mes témoignages que je leur ai enseignés, leurs fils aussi seront assis sur ton trône dans tous les siècles:
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
Parce que le Seigneur a élu Sion; il en a fait un choix privilégié pour sa demeure.
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
Ce sera mon repos dans les siècles des siècles; j'y résiderai, parce que je l'ai choisi avec prédilection.
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
Je bénirai et bénirai sa chasse; ses pauvres, je les rassasierai de pain.
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
Ses prêtres, je les revêtirai de salut, et ses saints tressailliront d'allégresse.
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
C'est là que j'élèverai le front de David, là que j'ai préparé une lampe pour mon Christ.
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
Pour ses ennemis, je les revêtirai de honte; mais sur lui fleurira ma sanctification.

< Zabura 132 >