< Zabura 132 >
1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
A SONG OF THE ASCENTS. Remember, YHWH, for David, all his afflictions;
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
Who has sworn to YHWH, He has vowed to the Mighty One of Jacob:
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
“If I enter into the tent of my house, If I go up on the couch of my bed,
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
If I give sleep to my eyes, To my eyelids—slumber,
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
Until I find a place for YHWH, dwelling places for the Mighty One of Jacob.”
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
Behold, we have heard it in Ephratah, We have found it in the fields of the forest.
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
We come into His dwelling places, We bow ourselves at His footstool.
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
Arise, O YHWH, to Your rest, You, and the Ark of Your strength,
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
Your priests put on righteousness, And Your pious ones cry aloud.
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
For the sake of Your servant David, Do not turn back the face of Your anointed.
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
YHWH has sworn truth to David, He does not turn back from it: “Of the fruit of your body, I set on the throne for you.
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
If your sons keep My covenant, And My testimonies that I teach them, Their sons also forever and ever Sit on the throne for you.”
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
For YHWH has fixed on Zion, He has desired [it] for a seat to Himself,
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
“This [is] My rest forever and ever, Here I sit, for I have desired it.
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
I greatly bless her provision, I satisfy her poor [with] bread,
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
And I clothe her priests [with] salvation, And her pious ones sing aloud.
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
There I cause a horn to spring up for David, I have arranged a lamp for My Anointed.
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
I clothe His enemies [with] shame, And His crown flourishes on Him!”