< Zabura 132 >

1 Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
Een bedevaartslied. Blijf David gedenken, o Jahweh, En alle moeite, die hij zich troostte,
2 Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
Omdat hij Jahweh had gezworen, Jakobs Sterke had beloofd:
3 “Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
Ik zal mijn woontent niet ingaan, Mijn legerstede niet beklimmen,
4 ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
Mijn ogen geen slaap gunnen, Mijn wimpers geen sluimer:
5 sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
Voordat ik een plaats heb gevonden voor Jahweh, Voor Jakobs Sterke een woning!
6 Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
Zie, wij hoorden, dat zij in Efráta was, Wij vonden haar weer in de velden van Jáar;
7 “Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
Laat ons naar zijn Woning gaan, En ons voor zijn voetbank werpen!
8 ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
Jahweh, trek op naar uw rustplaats, Gij zelf en de ark uwer glorie!
9 Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
Mogen uw priesters met gerechtigheid worden bekleed, En uw vromen een jubellied zingen!
10 Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
Om wille van David, uw dienaar, Wijs het gebed van uw gezalfde niet af!
11 Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
En Jahweh heeft aan David gezworen, Een trouwe Belofte, waarvan Hij niet afwijkt: Van de vrucht van uw schoot Zet Ik er een op uw troon!
12 in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
En zo uw zonen mijn verbond onderhouden, En de vermaningen, die Ik hun gaf, Dan zullen ook hùn zonen voor eeuwig Op uw troon blijven zitten!
13 Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
Want Jahweh heeft Sion verkoren, En Zich tot woning begeerd!
14 “Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
"Hij is mijn rustplaats voor eeuwig; Hier wil Ik wonen, want hèm heb Ik verkoren!
15 zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
Zijn mondkost zal Ik ruimschoots zegenen, Zijn armen verzadigen met brood;
16 Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
Zijn priesters zal Ik met heil bekleden. Zijn vromen zullen een jubellied zingen!
17 “A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
Hier zal Ik David een Hoorn doen ontspruiten, Een lamp ontsteken voor mijn Gezalfde;
18 Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
Zijn vijanden zal Ik met schande bedekken, Mijn kroon zal schitteren op zijn hoofd!"

< Zabura 132 >