< Zabura 131 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Zuciyata ba mai girman kai ba ce, ya Ubangiji, idanuna ba sa fariya; ban dami kaina da manyan al’amura ba ko abubuwan da suka sha ƙarfina.
“A psalm of the steps, or the goings up. Of David.” O LORD! my heart is not haughty, nor my eyes lofty; I employ not myself on great things, or things too wonderful for me!
2 Amma na haƙura na kuma kwantar da raina; kamar yaron da aka yaye tare da mahaifiyarsa, kamar yaron da aka yaye haka raina yake a cikina.
Yea, I have stilled and quieted my soul As a weaned child upon his mother; My soul within me is like a weaned child.
3 Ya Isra’ila, sa zuciyarka ga Ubangiji yanzu da har abada kuma.
O Israel! trust in the LORD, Henceforth even for ever!