< Zabura 130 >
1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
“A psalm of the steps, or the goings up.” Out of the depths do I cry to thee, O LORD!
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
O Lord! listen to my voice, Let thine ears be attentive to my supplication!
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
If thou, LORD, shouldst treasure up transgressions, Lord, who could stand?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
But with thee is forgiveness, That thou mayst be feared.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
I trust in the LORD; my soul doth trust, And in his promise do I confide.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
My soul waiteth for the LORD More than they who watch for the morning; Yea, more than they who watch for the morning!
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
O Israel! trust in the LORD! For with the LORD is mercy, And with him is plenteous redemption.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
He will redeem Israel From all his iniquities.