< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Cantique Mahaloth. Ô Éternel! je t'invoque des lieux profonds.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Seigneur, écoute ma voix! que tes oreilles soient attentives à la voix de mes supplications.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Ô Eternel! si tu prends garde aux iniquités, Seigneur, qui est-ce qui subsistera?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Mais il y a pardon par-devers toi, afin que tu sois craint.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
J'ai attendu l'Eternel; mon âme l'a attendu, et j'ai eu mon attente en sa parole.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Mon âme [attend] le Seigneur plus que les sentinelles [n'attendent] le matin, plus que les sentinelles [n'attendent] le matin.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israël, attends-toi à l'Eternel: car l'Eternel est miséricordieux et il y a rédemption en abondance par devers lui.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
Et lui-même rachètera Israël de toutes ses iniquités.

< Zabura 130 >