< Zabura 129 >

1 Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
Cantique de Mahaloth. Qu'Israël dise maintenant: ils m'ont souvent tourmenté dès ma jeunesse.
2 sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
Ils m'ont souvent tourmenté dès ma jeunesse; [toutefois] ils n'ont point encore été plus forts que moi.
3 Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
Des laboureurs ont labouré sur mon dos, ils y ont tiré tout au long leurs sillons.
4 Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
L'Eternel est juste; il a coupé les cordes des méchants.
5 Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
Tous ceux qui ont Sion en haine, rougiront de honte, et seront repoussés en arrière.
6 Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
Ils seront comme l'herbe des toits, qui est sèche avant qu'elle monte en tuyau;
7 da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
De laquelle le moissonneur ne remplit point sa main, ni celui qui cueille les javelles [n'en remplit] point ses bras;
8 Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Et [dont] les passants ne diront point: la bénédiction de l'Eternel soit sur vous; nous vous bénissons au nom de l'Eternel.

< Zabura 129 >