< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
A SONG OF THE ASCENTS. I have called You from the depths, YHWH.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Lord, listen to my voice, Your ears are attentive to the voice of my supplications.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
If You observe iniquities, Lord YAH, who stands?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
But forgiveness [is] with You, that You may be feared.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
I hoped [for] YHWH—my soul has hoped, And I have waited for His word.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
My soul [is] for the Lord, More than those watching for morning, Watching for morning!
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israel waits on YHWH, For kindness [is] with YHWH, And redemption [is] abundant with Him.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
And He redeems Israel from all his iniquities!

< Zabura 130 >