< Zabura 126 >
1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
Wallfahrtslieder. Als Jahwe das Geschick Zions wendete, waren wir wie Träumende.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Da war unser Mund voll Lachens, und unsere Zunge voll Jubels; da sprach man unter den Heiden: “Jahwe hat Großes an diesen gethan!”
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
Großes hatte Jahwe an uns gethan; wir waren fröhlich.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Wende, Jahwe, unser Geschick, gleich Rinnsalen im Südland.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Die unter Thränen säeten, werden mit Jubel ernten.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Unter beständigem Weinen geht man dahin und trägt den Samen zur Aussaat; mit Jubel kehrt man heim und trägt seine Garben!