< Zabura 122 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Wallfahrtslieder. Von David. Ich freute mich, als man zu mir sprach: “Laßt uns zum Tempel Jahwes gehn!”
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Unsere Füße stehen in deinen Thoren, Jerusalem!
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem, du wiedergebaute, wie eine Stadt, die allzumal zusammengefügt ist,
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
wohin die Stämme hinaufziehen, die Stämme Jahs, nach dem Gesetz für Israel, um dem Namen Jahwes zu danken.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Denn dort stehen Gerichtssessel, Sessel des Hauses Davids.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Erbittet Frieden für Jerusalem: Mögen Ruhe haben, die dich lieben.
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Friede sei in deinen Bollwerken, Ruhe in deinen Palästen.
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
Um meiner Brüder und Freunde willen laßt mich sprechen: Friede sei in dir!
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Um des Tempels Jahwes, unseres Gottes, willen will ich dein Bestes suchen.

< Zabura 122 >