< Zabura 126 >
1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
Une chanson d'ascension. Lorsque Yahvé ramena ceux qui étaient revenus à Sion, nous étions comme ceux qui rêvent.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Et notre bouche s'est remplie de rires, et notre langue avec des chants. Alors on dit parmi les nations, « Yahvé a fait de grandes choses pour eux. »
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
Yahvé a fait de grandes choses pour nous, et nous sommes heureux.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Rétablis notre fortune, Yahvé, comme les ruisseaux du Néguev.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Ceux qui sèment dans les larmes récolteront dans la joie.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Celui qui s'en va en pleurant, portant de la semence pour semer, reviendra certainement avec joie, portant ses gerbes.