< Zabura 125 >

1 Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
Une chanson d'ascension. Ceux qui se confient en Yahvé sont comme la montagne de Sion, qui ne peut pas être déplacé, mais qui reste pour toujours.
2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
Comme les montagnes entourent Jérusalem, Ainsi Yahvé entoure son peuple dès maintenant et pour toujours.
3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
Car le sceptre de la méchanceté ne restera pas sur le lot des justes, afin que les justes n'utilisent pas leurs mains pour faire le mal.
4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
Fais du bien, Yahvé, à ceux qui sont bons, à ceux qui sont droits dans leur cœur.
5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
Mais quant à ceux qui se détournent vers leurs voies tortueuses, Yahvé les emmènera avec les ouvriers de l'iniquité. Que la paix soit avec Israël.

< Zabura 125 >