< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
A Song of Ascents. When the LORD brought back those that returned to Zion, we were like unto them that dream.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Then was our mouth filled with laughter, and our tongue with singing; then said they among the nations: 'The LORD hath done great things with these.'
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
The LORD hath done great things with us; we are rejoiced.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Turn our captivity, O LORD, as the streams in the dry land.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
They that sow in tears shall reap in joy.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Though he goeth on his way weeping that beareth the measure of seed, he shall come home with joy, bearing his sheaves.

< Zabura 126 >