< Zabura 125 >

1 Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
[the] song of The ascents those [who] trust in Yahweh [are] like [the] mountain of Zion [which] not it will be shaken [which] for ever it will remain.
2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
Jerusalem mountains [are] around it and Yahweh [is] around people his from now and until perpetuity.
3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
For not it will rest [the] scepter of wickedness over [the] allotted portion of the righteous [people] so that not may stretch out the righteous [people] in injustice hands their.
4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
Do good! O Yahweh to the good [people] and to [people] upright in hearts their.
5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.
And those [who] turn aside twisting [ways] their he will lead away them Yahweh with [those who] do wickedness peace [be] on Israel.

< Zabura 125 >