< Zabura 122 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Пісня проча́н. Давидова.
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Ноги наші стояли в воро́тях Твоїх, Єрусали́ме.
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Єрусалиме, збудо́ваний ти як те місто, що злу́чене ра́зом,
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
куди схо́дять племе́на, племе́на Господні, — щоб сві́дчити Ізра́їлеві, щоб Іме́нню Господньому дя́кувати!
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Бо то там на престо́лах для суду сидять, на престолах дому Дави́дового.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Миру бажайте для Єрусалиму: „Нехай бу́дуть безпе́чні, хто любить тебе!“
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Нехай буде мир у твоїх передму́р'ях, безпе́ка в пала́тах твоїх!
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
Ради бра́тті моєї та дру́зів моїх я буду каза́ти: „Мир тобі!“
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Ради дому Господа, нашого Бога, я буду шукати для тебе добра́!

< Zabura 122 >