< Zabura 122 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Yo me alegraba cuando me decían: Vayamos a la Casa de Yavé.
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Nuestros pies están plantados dentro de tus puertas, Oh Jerusalén.
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalén está edificada Como una ciudad compacta,
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Adonde suben las tribus de YA, Según una Ordenanza para Israel, A dar gracias al Nombre de Yavé,
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Porque allá están establecidos tronos de juicio, Los tronos de la casa de David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Oren por la paz de Jerusalén: Que prosperen los que te aman,
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Que haya paz dentro de tus muros Y prosperidad dentro de tus palacios.
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
Por amor a mis hermanos y a mis amigos, diré ahora: Haya paz dentro de ti.
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Por amor a la Casa de Yavé nuestro ʼElohim, Oraré por tu bien.

< Zabura 122 >