< Zabura 122 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Cântico dos degraus, de Davi: Alegro-me com os que me dizem: Vamos à casa do SENHOR.
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Nossos pés estão [adentro] de tuas portas, ó Jerusalém.
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalém está edificada como uma cidade bem unida;
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Para onde as tribos sobem, as tribos do SENHOR, como testemunho de Israel, para agradecerem ao nome do SENHOR.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Porque ali estão as cadeiras do julgamento; as cadeiras da casa de Davi.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Orai pela paz de Jerusalém; prosperem os que te amam.
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Paz haja em teus muros, e prosperidade em tuas fortalezas.
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
Por meus irmãos e amigos, assim falarei: Paz haja em ti.
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Pela Casa do SENHOR nosso Deus, buscarei o bem para ti.

< Zabura 122 >