< Zabura 122 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
En sang ved festreisene; av David. Jeg gleder mig ved dem som sier til mig: Vi vil gå til Herrens hus.
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Våre føtter står i dine porter, Jerusalem!
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem, du velbyggede, lik en by som er tett sammenføiet,
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
hvor stammene drar op, Herrens stammer, efter en lov for Israel, for å prise Herrens navn!
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
For der er stoler satt til dom, stoler for Davids hus.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Bed om fred for Jerusalem! La det gå dem vel som elsker dig!
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Der være fred innen din voll, ro i dine saler!
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
For mine brødres og mine venners skyld vil jeg si: Fred være i dig!
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
For Herrens, vår Guds huses skyld vil jeg søke ditt beste.

< Zabura 122 >