< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Canticum graduum. Laetatus sum in his, quae dicta sunt mihi: In domum Domini ibimus.
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Stantes erant pedes nostri, in atriis tuis Ierusalem.
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Ierusalem, quae aedificatur ut civitas: cuius participatio eius in idipsum.
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Illuc enim ascenderunt tribus, tribus Domini: testimonium Israel ad confitendum nomini Domini.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Quia illic sederunt sedes in iudicio, sedes super domum David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Rogate quae ad pacem sunt Ierusalem: et abundantia diligentibus te.
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Fiat pax in virtute tua: et abundantia in turribus tuis.
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
Propter fratres meos, et proximos meos, loquebar pacem de te:
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Propter domum Domini Dei nostri, quaesivi bona tibi.