< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
(다윗의 시. 곧 성전에 올라가는 노래) 사람이 내게 말하기를 여호와의 집에 올라가자 할 때에 내가 기뻐하였도다
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
예루살렘아! 우리 발이 네 성문 안에 섰도다
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
예루살렘아! 너는 조밀한 성읍과 같이 건설되었도다
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
지파들 곧 여호와의 이름에 감사하려고 이스라엘의 전례대로 그리로 올라가는도다
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
거기 판단의 보좌를 두셨으니 곧 다윗 집의 보좌로다
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
예루살렘을 위하여 평안을 구하라 예루살렘을 사랑하는 자는 형통하리로다
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
네 성 안에는 평강이 있고 네 궁중에는 형통이 있을지어다
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
내가 내 형제와 붕우를 위하여 이제 말하리니 네 가운데 평강이 있을지어다
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
여호와 우리 하나님의 집을 위하여 내가 네 복을 구하리로다