< Zabura 122 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
שיר המעלות לדוד שמחתי באמרים לי-- בית יהוה נלך
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
עמדות היו רגלינו-- בשעריך ירושלם
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
ירושלם הבנויה-- כעיר שחברה-לה יחדו
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
ששם עלו שבטים שבטי-יה--עדות לישראל להדות לשם יהוה
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
כי שמה ישבו כסאות למשפט כסאות לבית דוד
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
שאלו שלום ירושלם ישליו אהביך
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
יהי-שלום בחילך שלוה בארמנותיך
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
למען אחי ורעי-- אדברה-נא שלום בך
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
למען בית-יהוה אלהינו-- אבקשה טוב לך

< Zabura 122 >