< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Ein Wallfahrtslied. Von David. Ich freue mich an denen, die zu mir sagen: Lasset uns zum Hause des HERRN gehen!
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Unsre Füße stehen in deinen Toren, Jerusalem!
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem, du bist gebaut als eine Stadt, die fest in sich geschlossen ist,
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
wohin die Stämme hinaufziehen, die Stämme des HERRN (ein Zeugnis für Israel), zu preisen den Namen des HERRN!
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Denn dort sind Stühle gesetzt zum Gericht, die Stühle des Hauses David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Bittet für den Frieden Jerusalems! Es gehe wohl denen, die dich lieben!
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Friede sei in deinen Mauern und Glück in deinen Palästen!
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
Um meiner Brüder und Freunde willen sage ich: Friede sei in dir!
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Um des Hauses des HERRN, unsres Gottes, willen will ich dein Bestes suchen!