< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Cantique des pèlerinages. — De David. Je me réjouis quand on me dit: «Allons à la maison de l'Éternel!»
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Nos pas s'arrêtent Dans tes portes, ô Jérusalem,
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jérusalem, ville rebâtie. Dont les murailles n'ont plus de brèche!
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
C'est là que montent les tribus, les tribus de l'Éternel, Selon la loi donnée à Israël, Pour célébrer le nom de l'Éternel.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
C'est là que sont dressés les trônes de la justice. Les trônes de la maison de David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Priez pour la paix de Jérusalem! Que ceux qui t'aiment vivent en sécurité!
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Que la paix soit dans tes murs. Et la sécurité dans tes palais!
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
Pour l'amour de mes frères et de mes amis, J'invoque la paix sur toi.
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Par amour pour la maison de l'Éternel, notre Dieu, Je demande pour toi le bonheur!