< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Cantique des montées. De David. J’ai été dans la joie quand on m’a dit: « Allons à la maison de Yahweh! »
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Enfin! Nos pieds s’arrêtent à tes portes, Jérusalem!
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jérusalem, tu es bâtie comme une ville où tout se tient ensemble.
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Là montent les tribus, les tribus de Yahweh, selon la loi d’Israël, pour louer le nom de Yahweh.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Là sont établis des sièges pour le jugement, les sièges de la maison de David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Faites des vœux pour Jérusalem: Qu’ils soient heureux ceux qui t’aiment!
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Que la paix règne dans tes murs, la prospérité dans tes palais!
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
A cause de mes frères et de mes amis, je demande pour toi la paix;
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
à cause de la maison de Yahweh, notre Dieu, je désire pour toi le bonheur.