< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
A Song of Ascents. David’s. I was glad, when they were saying unto me, Unto the house of Yahweh, let us go!
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Standing are our feet, within thy gates, O Jerusalem!
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem! that hath been builded, A true city, all joined together as one:
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Whither have come up the tribes, The tribes of Yah, A testimony to Israel, To give thanks unto the Name of Yahweh:
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
For there are set—Thrones for justice, Thrones for the house David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Ask ye for the peace of Jerusalem, They shall prosper, who love thee!
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Peace be within thy walls, prosperity within thy palaces:
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
For the sake of my brethren and friends, Oh, might I speak [saying], Peace be within thee!
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
For the sake of the house of Yahweh our God, will I seek blessing for thee.