< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
“A psalm of the steps, or the goings up. By David.” I was glad when they said to me, Let us go up to the house of the LORD!
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Our feet are standing Within thy gates, O Jerusalem!
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem, the rebuilt city! The city that is joined together!
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Thither the tribes go up, The tribes of the LORD, according to the law of Israel, To praise the name of the LORD.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
There stand the thrones of judgment, The thrones of the house of David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Pray for the peace of Jerusalem! May they prosper who love thee!
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Peace be within thy walls, And prosperity within thy palaces!
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
For my brethren and companions' sake will I say, Peace be within thee!
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
For the sake of the house of the LORD, our God, Will I seek thy good!