< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
A Song of Ascents; of David. I rejoiced when they said unto me: 'Let us go unto the house of the LORD.'
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Our feet are standing within thy gates, O Jerusalem;
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem, that art builded as a city that is compact together;
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Whither the tribes went up, even the tribes of the LORD, as a testimony unto Israel, to give thanks unto the name of the LORD.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
For there were set thrones for judgment, the thrones of the house of David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Pray for the peace of Jerusalem; may they prosper that love thee.
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Peace be within thy walls, and prosperity within thy palaces.
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
For my brethren and companions' sakes, I will now say: 'Peace be within thee.'
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
For the sake of the house of the LORD our God I will seek thy good.