< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
I rejoiced at the things that were said to me: We shall go into the house of the Lord.
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Our feet were standing in thy courts, O Jerusalem.
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem, which is built as a city, which is compact together.
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
For thither did the tribes go up, the tribes of the Lord: the testimony of Israel, to praise the name of the Lord.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Because their seats have sat in judgment, seats upon the house of David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Pray ye for the things that are for the peace of Jerusalem: and abundance for them that love thee.
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Let peace be in thy strength: and abundance in thy towers.
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
For the sake of my brethren, and of my neighbours, I spoke peace of thee.
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Because of the house of the Lord our God, I have sought good things for thee.