< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
A Song of Degrees. I was glad when they said to me, Let us go into the house of the Lord.
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Our feet stood in your courts, O Jerusalem.
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem is built as a city whose fellowship is complete.
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
For there the tribes went up, the tribes of the Lord, as a testimony for Israel, to give thanks to the name of the Lord.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
For there are set thrones for judgement, [even] thrones for the house of David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Pray now for the peace of Jerusalem: and [let there be] prosperity to them that love you.
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Let peace, I pray, be within your host, and prosperity in your palaces.
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
For the sake of my brethren and my neighbours, I have indeed spoken peace concerning you.
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Because of the house of the Lord our God, I have diligently sought your good.