< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
A song of ascents. Of David. I was glad when they said to me, “Let us go to the house of the LORD.”
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Our feet are standing in your gates, O Jerusalem.
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem is built up as a city united together,
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
where the tribes go up, the tribes of the LORD, as a testimony for Israel, to give thanks to the name of the LORD.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
For there the thrones of judgment stand, the thrones of the house of David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Pray for the peace of Jerusalem: “May those who love you prosper.
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
May there be peace within your walls, and prosperity inside your fortresses.”
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
For the sake of my brothers and friends, I will say, “Peace be within you.”
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
For the sake of the house of the LORD our God, I will seek your prosperity.