< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
Jeg opløfter mine Øjne til Bjergene; hvorfra skal min Hjælp komme?
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
Min Hjælp kommer fra Herren, som skabte Himmelen og Jorden.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Han tillade ikke din Fod at snuble, og han, som bevarer dig, slumre ikke!
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Se, han slumrer ikke og sover ikke, han, som bevarer Israel!
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
Herren er den, der bevarer dig; Herren er din Skygge ved din højre Haand.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
Solen skal ikke stikke dig om Dagen eller Maanen om Natten.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Herren skal bevare dig fra alt ondt, han skal bevare din Sjæl.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Herren skal bevare din Udgang og din Indgang fra nu af og indtil evig Tid.

< Zabura 121 >