< Zabura 31 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
Til Sangmesteren; en Psalme af David. Herre! jeg tror paa dig, lad mig ikke beskæmmes evindelig; udfri mig ved din Retfærdighed.
2 Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
Bøj dit Øre til mig, red mig hastelig; vær mig en fast Klippe, en sikker Borg til at frelse mig.
3 Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
Thi du er min Klippe og min Befæstning, og for dit Navns Skyld vil du lede mig og føre mig.
4 Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
Du vil udføre mig af Garnet, som de have skjult for mig; thi du er min Styrke.
5 Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
I din Haand befaler jeg min Aand; du forløste mig, Herre, du sande Gud!
6 Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
Jeg hader dem, som tage Vare paa Løgnens Gøglebilleder; men paa Herren forlader jeg mig.
7 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
Jeg vil fryde mig og være glad ved din Miskundhed; thi du har set min Elendighed, du har kendt min Sjæleangest.
8 Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
Du overantvordede mig ikke i Fjendens Haand; du lod mine Fødder staa paa et vidt Rum.
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
Herre! vær mig naadig, thi jeg er angest; hentæret af Sorg er mit Øje, min Sjæl og min Krop.
10 Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
Thi mit Liv er svundet hen i Bedrøvelse og mine Aar i Suk; min Kraft er brudt for min Misgernings Skyld, og mine Ben ere hentørrede.
11 Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
Ved alle mine Fjender er jeg bleven til Spot, og det i rigt Maal for mine Naboer og til Forskrækkelse for mine Kyndinge; de, som saa mig udenfor, flyede fra mig.
12 An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
Jeg blev glemt, ude af Sinde som en død, jeg var som et Kar, der gaar tabt.
13 Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
Thi jeg hørte manges Bagtalelse, der var Rædsel trindt omkring; idet de raadsloge sammen over mig, tænkte de at tage Livet af mig.
14 Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
Men jeg forlader mig paa dig, Herre! jeg sagde: Du er min Gud.
15 Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
Mine Tider ere i din Haand; red mig fra mine Fjenders Haand og fra dem, som forfølge mig.
16 Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
Lad dit Ansigt lyse over din Tjener; frels mig ved din Miskundhed.
17 Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol h7585)
Herre! lad mig ikke beskæmmes, thi jeg har kaldt paa dig; lad de ugudelige beskæmmes, lad dem tie i Dødsriget. (Sheol h7585)
18 Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
Lad de falske Læber blive stumme, som tale frækt i Hovmod og Foragt imod den retfærdige.
19 Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
Hvor stor er din Godhed, som du har gemt for dem, som dig frygte, hvilken du har udvist imod dem, som tro paa dig, for Menneskens Børn.
20 Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
Du vil skjule dem i dit Ansigts Skjul for Menneskers Sammensværgelser; du vil gemme dem i en Hytte for Tungers Kiv.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
Lovet være Herren! thi han har underligt bevist sin Miskundhed imod mig i en fast Stad.
22 Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
Og jeg sagde, der jeg var forfærdet: Jeg er udryddet fra dine Øjne; men du hørte mine ydmyge Begæringers Røst, da jeg raabte til dig.
23 Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
Elsker Herren, alle hans hellige! Herren bevarer de trofaste og betaler i Overmaal ham, som øver Hovmod.
24 Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.
Værer frimodige, og han skal styrke eders Hjerte, alle I, som haabe paa Herren!

< Zabura 31 >