< Zabura 118 >
1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
¡Hallelú Yah! Alabad a Yahvé porque es bueno, porque su misericordia permanece para siempre.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Diga ahora la casa de Israel: “Su misericordia permanece para siempre.”
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Diga la casa de Aarón: “Su misericordia permanece para siempre.”
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Digan los que temen a Yahvé: “Su misericordia permanece para siempre.”
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
En la estrechez invoqué a Yah; y Yah me escuchó y me sacó a la anchura.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Yahvé está en mi favor, nada temo. ¿Qué podrá hacerme el hombre?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Yahvé, mi auxiliador, está conmigo y miraré (confundidos) a mis enemigos.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Mejor es acogerse a Yahvé que confiar en el hombre.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Mejor es acogerse a Yahvé que confiar en príncipes.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Todas las naciones me habían cercado; en el Nombre de Yahvé las hice pedazos.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Me envolvieron por todas partes; en el Nombre de Yahvé las hice pedazos.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Me rodeaban como abejas, ardían como fuego de espinas; en el Nombre de Yahvé las hice pedazos.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Empujado, empujado, estuve a punto de caer, pero Yahvé vino en mi ayuda.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Mi fuerza y mi valor es Yahvé, mi Salvador es Él.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Voz de exultación y de triunfo en las tiendas de los justos: “La diestra de Yahvé ha hecho proezas;
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
la diestra de Yahvé se alzó muy alto, la diestra de Yahvé ha hecho proezas.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
No moriré, sino que viviré; y publicaré las hazañas de Yahvé.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Me castigó Yah, me castigó, pero no me entregó a la muerte.”
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Abridme las puertas de la justicia, para que entre por ellas y dé gracias a Yah.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Esta es la puerta de Yahvé; entren los justos por ella.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Te daré gracias porque me escuchaste y te has hecho mi Salvador.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
La piedra que rechazaron los constructores ha venido a ser la piedra angular.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
Obra de Yahvé es esto, admirable ante nuestros ojos.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Este es el día que hizo Yahvé; alegrémonos por él y celebrémoslo.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Sí, oh Yahvé, ¡da la victoria! Sí, oh Yahvé, ¡da prosperidad!
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Bendito el que viene en el nombre de Yahvé; desde la casa de Yahvé os bendecimos.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Yahvé es Dios y nos ha iluminado. Ordenad procesión con ramos frondosos hasta los cuernos del altar.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Mi Dios eres Tú y te doy gracias; mi Dios eres Tú, quiero alabarte;
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alabad a Yahvé porque es bueno; porque su misericordia permanece para siempre.