< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Praise yee the Lord, because he is good: for his mercie endureth for euer.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let Israel now say, That his mercy endureth for euer.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let the house of Aaron nowe say, That his mercy endureth for euer.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let them, that feare the Lord, nowe say, That his mercie endureth for euer.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
I called vpon the Lord in trouble, and the Lord heard me, and set me at large.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
The Lord is with mee: therefore I will not feare what man can doe vnto me.
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
The Lord is with mee among them that helpe me: therefore shall I see my desire vpon mine enemies.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
It is better to trust in the Lord, then to haue confidence in man.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
It is better to trust in the Lord, then to haue confidence in princes.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
All nations haue compassed me: but in the Name of the Lord shall I destroy them.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They haue compassed mee, yea, they haue compassed mee: but in the Name of the Lord I shall destroy them.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They came about mee like bees, but they were quenched as a fire of thornes: for in the Name of the Lord I shall destroy them.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Thou hast thrust sore at me, that I might fall: but the Lord hath holpen me.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
The Lord is my strength and song: for he hath beene my deliuerance.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
The voice of ioy and deliuerance shall be in the tabernacles of the righteous, saying, The right hand of the Lord hath done valiantly.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
The right hand of the Lord is exalted: the right hand of the Lord hath done valiantly.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
I shall not die, but liue, and declare the woorkes of the Lord.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
The Lord hath chastened me sore, but he hath not deliuered me to death.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Open ye vnto me the gates of righteousnes, that I may goe into them, and praise the Lord.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
This is the gate of the Lord: the righteous shall enter into it.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
I will praise thee: for thou hast heard mee, and hast beene my deliuerance.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
The stone, which the builders refused, is the head of the corner.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
This was the Lordes doing, and it is marueilous in our eyes.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
This is the day, which the Lord hath made: let vs reioyce and be glad in it.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
O Lord, I praie thee, saue now: O Lord, I praie thee nowe giue prosperitie.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Blessed be he, that commeth in the Name of the Lord: wee haue blessed you out of the house of the Lord.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
The Lord is mightie, and hath giuen vs light: binde the sacrifice with cordes vnto the hornes of the altar.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Thou art my God, and I will praise thee, euen my God: therefore I will exalt thee.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Praise ye the Lord, because he is good: for his mercie endureth for euer.

< Zabura 118 >