< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
I love Yahweh, because he hears me when I cry for him to help me.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
He listens to me, so I will call out to him all during my life.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Everything around me [MET] caused me to think that I would die; I was very afraid that I would [die and go to] the place where dead people are. I was very distressed/worried and afraid. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
[But] then I called out to Yahweh, saying, “Yahweh, I plead with you to save/rescue me!”
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Yahweh is kind and does what is right; he is our God, and he acts mercifully [to us].
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
He protects those who (are helpless/cannot defend themselves); and when I thought that I would die, he saved me.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
I must encourage/tell myself to (have inner peace/not worry any more), because Yahweh has done very good things for me.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Yahweh has saved me [SYN] from dying, and has kept/protected me from [troubles that would cause me to] cry. He has kept/protected me from stumbling.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
[So here] on the earth, where people are still alive, I live knowing that Yahweh is [directing] me.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
I continued to believe/trust [in Yahweh], even when I said, “I am greatly afflicted/troubled.”
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
[Even] when I was distressed/worried and said, “I cannot trust anyone,” [I continued to trust in Yahweh].
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
So now [I will tell you] [RHQ] what I will offer to Yahweh, because of all the good things that he has done for me.
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
I will offer to him a cup [of wine] to thank him for saving/rescuing me.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
When I am together with many [HYP] people who belong to Yahweh, I will give to him the offerings that I solemnly promised to give to him.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Yahweh is very grieved/sad when one of his people dies.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
I am one of those who serve Yahweh; I serve him like my mother did. He has freed/saved me from dying (OR, from being fastened by chains).
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
[So] I will offer to him a sacrifice to thank him, and I will pray to him.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
When I am together with many of [HYP] the people who belong to Yahweh, [in the courtyard] outside his temple in Jerusalem, I will give to him the offerings that I solemnly promised to give to him. Praise Yahweh!
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Zabura 116 >