< Zabura 113 >

1 Yabi Ubangiji. Ku yabe shi, ya ku bayin Ubangiji, ku yabi sunan Ubangiji.
Hallelujah. Praise, O ye servants of the LORD, praise the name of the LORD.
2 Bari a yabi sunan Ubangiji, yanzu da har abada kuma.
Blessed be the name of the LORD from this time forth and for ever.
3 Daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa, a yabi sunan Ubangiji.
From the rising of the sun unto the going down thereof the LORD'S name is to be praised.
4 Ana ɗaukaka Ubangiji a bisa dukan al’ummai, ɗaukakarsa a bisa sammai
The LORD is high above all nations, His glory is above the heavens.
5 Wane ne yake kamar Ubangiji Allahnmu, Wannan mai zama a kursiyi can bisa,
Who is like unto the LORD our God, that is enthroned on high,
6 wanda yake sunkuya yă dubi sammai da duniya?
That looketh down low upon heaven and upon the earth?
7 Yakan tā da matalauta daga ƙura yakan ɗaga mabukata daga tarin toka;
Who raiseth up the poor out of the dust, and lifteth up the needy out of the dunghill;
8 ya zaunar da su tare da sarakuna, tare da sarakunan mutanensu.
That He may set him with princes, even with the princes of His people.
9 Yakan zaunar da matar da ba haihuwa a gidanta ta zama kamar mahaifiyar’ya’ya mai farin ciki. Yabi Ubangiji.
Who maketh the barren woman to dwell in her house as a joyful mother of children. Hallelujah.

< Zabura 113 >