< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alabád a Jehová, porque es bueno: porque para siempre es su misericordia.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
¿Quién dirá las valentías de Jehová? ¿ quién contará sus alabanzas?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Dichosos los que guardan juicio, los que hacen justicia en todo tiempo.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Acuérdate de mí, o! Jehová, en la voluntad de tu pueblo: visítame con tu salud;
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Para que yo vea el bien de tus escogidos: para que me alegre en la alegría de tu gente: y me gloríe con tu heredad.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Pecamos con nuestros padres, hicimos iniquidad, hicimos impiedad.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Nuestros padres en Egipto no entendieron tus maravillas: no se acordaron de la muchedumbre de tus misericordias: mas se rebelaron sobre la mar, en el mar Bermejo.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Y salvólos por su nombre: para hacer notoria su fortaleza.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Y reprendió al mar Bermejo, y secóse: e hízolos ir por el abismo, como por un desierto.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Y salvólos de mano del enemigo: y rescatólos de mano del adversario.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Y cubrieron las aguas a sus enemigos: uno de ellos no quedó.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Y creyeron a sus palabras: y cantaron su alabanza.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Apresuráronse, olvidáronse de sus obras: no esperaron en su consejo.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Y desearon mal deseo en el desierto: y tentaron a Dios en la soledad.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Y él les dio lo que pidieron: y envió flaqueza en sus almas.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Y tomaron zelo contra Moisés en el campo: contra Aarón santo de Jehová.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Abrióse la tierra, y tragó a Datán, y cubrió a la compañía de Abirom.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Y encendióse el fuego en su compañía: la llama quemó a los impíos.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Hicieron el becerro en Horeb: y encorváronse a un vaciadizo.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Y trocaron su gloria por la imagen de un buey, que come yerba.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Olvidaron al Dios de su salud: que había hecho grandezas en Egipto,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Maravillas en la tierra de Cam, temerosas cosas sobre el mar Bermejo.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Y trató de destruirlos, si Moisés su escogido no se pusiera al portillo delante de él: para apartar su ira para que no los destruyese.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Y aborrecieron la tierra deseable: no creyeron a su palabra.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Y murmuraron en sus tiendas; y no oyeron la voz de Jehová.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Y alzó su mano para ellos; para postrarlos en el desierto,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
Y para postrar su simiente entre las naciones; y esparcirlos por las tierras.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Y allegáronse a Baal-pehor; y comieron los sacrificios de los muertos.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Y ensañáron le con sus obras; y aumentó en ellos la mortandad.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Y púsose Finees, y juzgó; y la mortandad cesó.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Y fuéle contado a justicia de generación a generación para siempre.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Y ensañáron le a las aguas de Meriba; e hizo mal a Moisés por causa de ellos.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Porque hicieron rebelar a su espíritu, y habló inconsideradamente con sus labios.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
No destruyeron los pueblos, que Jehová les dijo:
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Antes se envolvieron con los Gentiles; y aprendieron sus obras:
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Y sirvieron a sus ídolos: los cuales les fueron por ruina.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Y sacrificaron sus hijos y sus hijas a los demonios.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Y derramaron la sangre inocente: la sangre de sus hijos y de sus hijas, que sacrificaron a los ídolos de Canaán; y la tierra fue contaminada con sangres.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Y contamináronse con sus obras, y fornicaron con sus hechos.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Y encendióse el furor de Jehová sobre su pueblo; y abominó su heredad.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Y entrególos en poder de los Gentiles; y enseñoreáronse de ellos los que les aborrecían.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Y sus enemigos les oprimieron, y fueron quebrantados debajo de su mano.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Muchas veces los escapó, y ellos se rebelaron a su consejo; y fueron humillados por su maldad.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Mas él miraba, cuando estaban en angustia, oyendo su clamor.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Y acordábase de su concierto con ellos, y arrepentíase conforme a la muchedumbre de sus miseraciones.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Y hacía que tuviesen de ellos misericordia todos los que los tenían cautivos.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Sálvanos Jehová Dios nuestro, y júntanos de entre las naciones, para que loemos tu santo nombre, para que nos gloriemos de tus alabanzas.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Bendito Jehová Dios de Israel desde el siglo y hasta el siglo; y diga todo el pueblo: Amén, Alelu- Jah.