< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Alabád a Jehová, invocád su nombre: hacéd notorias sus obras en los pueblos.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Cantád a él, decíd salmos a él: hablád de todas sus maravillas.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Gloriáos en su nombre santo: alégrese el corazón de los que buscan a Jehová.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Buscád a Jehová, y a su fortaleza: buscád su rostro siempre.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Acordáos de sus maravillas, que hizo: de sus prodigios, y de los juicios de su boca,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
Simiente de Abraham su siervo: hijos de Jacob sus escogidos.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
El es Jehová nuestro Dios: en toda la tierra están sus juicios.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Acordóse para siempre de su alianza: de la palabra que mandó para mil generaciones:
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
La cual concertó con Abraham, y de su juramento a Isaac.
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
Y establecióla a Jacob por decreto, a Israel por concierto eterno,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Diciendo: A ti daré la tierra de Canaán, por cordel de vuestra heredad.
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Siendo ellos pocos hombres en número, y extranjeros en ella.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Y anduvieron de gente en gente: de un reino a otro pueblo.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
No consintió que hombre los agraviase: y por causa de ellos castigó a los reyes.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
No toquéis en mis ungidos: ni hagáis mal a mis profetas.
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Y llamó a la hambre sobre la tierra: y toda fuerza de pan quebrantó.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Envió un varón delante de ellos: por siervo fue vendido José.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
Afligieron sus pies con grillos: en hierro entró su persona,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Hasta la hora que llegó su palabra: el dicho de Jehová le purificó.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Envió el rey, y soltóle: el señor de los pueblos, y le desató.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Púsole por señor de su casa: y por enseñoreador en toda su posesión.
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
Para echar presos sus príncipes, como él quisiese; y enseñó sabiduría a sus viejos.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Y entró Israel en Egipto: y Jacob fue extranjero en la tierra de Cam.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
E hizo crecer su pueblo en gran manera: e hízole fuerte más que sus enemigos.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Volvió el corazón de ellos, para que aborreciesen a su pueblo: para que pensasen mal contra sus siervos.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Envió a su siervo Moisés: a Aarón, al cual escogió.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Pusieron en ellos las palabras de sus señales, y sus prodigios en la tierra de Cam.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Echó tinieblas, e hizo oscuridad, y no fueron rebeldes a su palabra.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Volvió sus aguas en sangre, y mató sus pescados.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Engendró ranas su tierra en las camas de sus reyes.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Dijo, y vino una mezcla de diversas moscas, piojos en todo su término.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Volvió sus lluvias en granizo: en fuego de llamas en su tierra.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
E hirió sus viñas, y sus higueras; y quebró los árboles de su término.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Dijo, y vino langosta, y pulgón sin número;
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
Y comió toda la yerba de su tierra, y comió el fruto de su tierra.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
E hirió a todos los primogénitos en su tierra, el principio de toda su fuerza.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Y sacólos con plata y oro; y no hubo en sus tribus enfermo.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egipto se alegró en su salida; porque había caído sobre ellos el terror de ellos.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Extendió una nube por cubierta, y fuego para alumbrar la noche.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Pidieron, e hizo venir codornices; y de pan del cielo les hartó.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Abrió la peña, y corrieron aguas; fueron por las securas como un río.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Porque se acordó de su santa palabra con Abraham su siervo.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Y sacó a su pueblo con gozo; con júbilo a sus escogidos.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
Y dióles las tierras de los Gentiles: y los trabajos de las naciones heredaron:
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
Para que guardasen sus estatutos; y conservasen sus leyes. Alelu- Jah.