< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Hvalite Gospoda. O zahvaljujte se Gospodu, ker je dober, kajti njegovo usmiljenje traja večno.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Kdo lahko izreče mogočna Gospodova dela? Kdo lahko naznanja vso njegovo hvalo?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Blagoslovljeni so tisti, ki se držijo sodbe in tisti, ki ob vseh časih ravna pravično.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Spomni se me, oh Gospod, z naklonjenostjo, ki jo prinašaš svojemu ljudstvu. Oh obišči me s svojo rešitvijo duše,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
da lahko vidim dobro tvojega izbranca, da se lahko veselim v veselju tvojega naroda, da se lahko ponašam s tvojo dediščino.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Grešili smo s svojimi očeti, zagrešili smo krivičnost, ravnali smo zlobno.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Naši očetje v Egiptu niso razumeli tvojih čudežev, niso se spominjali množice tvojih milosti, temveč so ga dražili pri morju, celó pri Rdečem morju.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Pa vendar jih je rešil zaradi svojega imena, da je lahko storil, da se spozna njegova mogočna moč.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Oštel je tudi Rdeče morje in le-to se je posušilo, tako jih je vodil skozi globine kakor skozi divjino.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Rešil jih je iz roke tistega, ki jih je sovražil in jih odkupil iz sovražnikove roke.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Vode so pokrile njihove sovražnike; niti eden izmed njih ni preostal.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Potem so verjeli njegovim besedam; peli so njegovo hvalo.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Kmalu so pozabili njegova dela, niso čakali na njegov nasvet,
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
temveč so silno hrepeneli v divjini in skušali Boga v puščavi.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Dal jim je njihovo zahtevo, toda poslal je pustost v njihove duše.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Zavidali so tudi Mojzesu v taboru in Aronu, Gospodovemu svetemu.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Zemlja se je odprla in požrla Datána in pokrila Abirámovo druščino.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
V njuni druščini pa je bil vžgan ogenj, plamen je požgal zlobne.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Naredili so tele na Horebu in oboževali ulito podobo.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Tako so svojo slavo zamenjali v podobnost vola, ki jé travo.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Pozabili so Boga, svojega rešitelja, ki je v Egiptu storil velike stvari,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
čudovita dela v Hamovi deželi in strašne stvari pri Rdečem morju.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Zato je rekel, da jih bo uničil, če ne bi njegov izbranec Mojzes stal pred njim v vrzeli, da odvrne njegov bes, da jih ne bi uničil.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Da, prezirali so prijetno deželo, niso verovali njegovi besedi,
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
temveč so godrnjali v svojih šotorih in niso prisluhnili Gospodovemu glasu.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Zato je dvignil svojo roko zoper njih, da jih zruši v divjini,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
da uniči njihovo seme tudi med narodi in da jih razkropi po deželah.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Pridružili so se tudi k Báal Peórju in jedli žrtvovanje mrtvim.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Tako so ga s svojimi domiselnostmi dražili do jeze, in mednje je vdrla nadloga.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Potem se je dvignil Pinhás in izvršil sodbo in tako se je nadloga zaustavila.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
To mu je bilo šteto v pravičnost, vsem rodovom na vékomaj.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Jezili so ga tudi pri vodah prepira, tako da se je zaradi njih za Mojzesa slabo izteklo,
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
ker so dražili njegovega duha, tako da je s svojimi ustnicami nepremišljeno govoril.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Niso pokončali narodov, glede katerih jim je Gospod zapovedal,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
temveč so bili pomešani med pogane in se naučili njihovih del.
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Služili so svojim malikom, ki so bili zanje past.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Da, svoje sinove in svoje hčere so žrtvovali hudičem
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
in prelivali nedolžno kri, celó kri svojih sinov in svojih hčera, ki so jih žrtvovali kánaanskim malikom, in dežela je bila oskrunjena s krvjo.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Tako so bili omadeževani s svojimi lastnimi deli in se šli vlačuganje s svojo lastno domiselnostjo.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Zato je bil zoper njegovo ljudstvo vžgan Gospodov bes, do take mere, da je preziral svojo lastno dediščino.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Izročil jih je v roko poganov in tisti, ki so jih sovražili, so vladali nad njimi.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Tudi njihovi sovražniki so jih zatirali in privedeni so bili v podjarmljenje, pod njihovo roko.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Mnogokrat jih je osvobodil, toda dražili so ga s svojo namero in bili so ponižani zaradi svoje krivičnosti.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Vendar ko je slišal njihovo vpitje, se je ozrl na njihovo stisko
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
in zanje se je spomnil svoje zaveze in se pokesal glede na množico svojih usmiljenj.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Pripravil jim je tudi usmiljenje pred vsemi tistimi, ki so jih odvedli ujete.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Reši nas, oh Gospod, naš Bog in zberi nas izmed poganov, da se zahvaljujemo tvojemu svetemu imenu in da zmagujemo v tvojem hvaljenju.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Blagoslovljen bodi Gospod, Izraelov Bog, od večnosti do večnosti in vse ljudstvo naj reče: »Amen. Hvalite Gospoda.«