< Zabura 105 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Oh zahvaljujte se Gospodu, kličite njegovo ime; med ljudstvom razglašajte njegova dela.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Prepevajte mu, prepevajte mu psalme, govorite o vseh njegovih čudovitih delih.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Ponašajte se z njegovim svetim imenom; naj se razveseljuje srce tistih, ki iščejo Gospoda.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Iščite Gospoda in njegovo moč; vselej iščite njegov obraz.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Spominjajte se njegovih čudovitih del, ki jih je storil, njegovih čudežev in sodb njegovih ust,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
oh, vi seme Abrahama, njegovega služabnika, vi otroci Jakoba, njegovega izbranca.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
On je Gospod, naš Bog; njegove sodbe so po vsej zemlji.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Na veke se spominja svoje zaveze, besede, ki jo je zapovedal tisočêrim rodovom.
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
Katero zavezo je sklenil z Abrahamom in svojo prisego Izaku
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
in isto potrdil Jakobu za zakon in Izraelu za večno zavezo,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
rekoč: »Tebi bom dal kánaansko deželo, žreb vaše dediščine, «
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
ko jih je bilo po številu le malo ljudi, da, zelo malo in tujci v njej.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Ko so hodili od enega naroda k drugemu, od enega kraljestva k drugemu ljudstvu
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
nobenemu človeku ni pustil, da jim stori krivico; da, zaradi njih je grajal kralje,
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
rekoč: »Ne dotikajte se mojih maziljencev in mojim prerokom ne delajte hudega.«
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Poleg tega je nad deželo poklical lakoto; zlomil je celotno oporo kruha.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
Pred njimi je poslal človeka, celó Jožefa, ki je bil prodan za služabnika,
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
katerega stopala so poškodovali z okovi, položen je bil v železo
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
do časa, ko je prišla njegova beseda; Gospodova beseda ga je prečistila.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Kralj je poslal in ga izpustil, celó vladar ljudstva in ga osvobodil.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Postavil ga je [za] gospodarja svoje hiše in vladarja vsega svojega imetja,
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
da po svoji mili volji zveže njegove prince in njegove senatorje uči modrosti.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Tudi Izrael je prišel v Egipt in Jakob je začasno prebival v Hamovi deželi.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Silno je pomnožil svoje ljudstvo in jih naredil močnejše kakor njihove sovražnike.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Njihovo srce je obrnil, da sovraži njegovo ljudstvo, da premeteno postopa z njegovimi služabniki.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Poslal je svojega služabnika Mojzesa in Arona, ki ga je izbral.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Prikazovala sta njegova znamenja med njimi in čudeže v Hamovi deželi.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Poslal je temo in jo naredil temačno in nista se uprla zoper njegovo besedo.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Njihove vode je spremenil v kri in njihove ribe usmrtil.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Njihova dežela je po sobah njihovih kraljev porodila žab v obilju.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Rekel je in prišle so različne vrste muh in uši po vseh njihovih krajih.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Dal jim je točo za dež in ognjen ogenj po njihovi deželi.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Udaril je tudi njihove trte in njihova figova drevesa in zlomil drevesa njihovih krajev.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Spregovoril je in prišle so leteče kobilice in gosenice in to brez števila,
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
pojedle so vsa njihova zelišča po celotni deželi in požrle sad njihovih tal.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Udaril je tudi vse prvorojence v njihovi deželi, vodilne izmed vse njihove moči.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Izpeljal jih je tudi s srebrom in zlatom, in med njihovimi rodovi ni bilo niti ene slabotne osebe.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egipt je bil vesel, ko so odšli, kajti strah pred njimi je padel nanje.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Razprostrl je oblak za pokrivalo in ogenj, da daje svetlobo v noči.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Ljudje so prosili in privedel je prepelice ter jih nasičeval z nebeškim kruhom.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Odprl je skalo in pridrle so vode, po suhih krajih so tekle kakor reka.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Kajti spomnil se je svoje svete obljube in Abrahama, svojega služabnika.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Svoje ljudstvo je izpeljal z radostjo in svoje izvoljene z veseljem
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
in jim dal dežele poganov in podedovali so trud ljudstev,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
da bi se lahko držali njegovih zakonov in obeleževali njegove postave. Hvalite Gospoda.