< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Zaburi ya Daudi. Ee nafsi yangu, umhimidi Bwana. Vyote vilivyomo ndani yangu vilihimidi jina lake takatifu.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Ee nafsi yangu, umhimidi Bwana, wala usisahau wema wake wote,
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
akusamehe dhambi zako zote, akuponya magonjwa yako yote,
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
aukomboa uhai wako na kaburi, akuvika taji ya upendo na huruma,
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
atosheleza mahitaji yako kwa vitu vyema, ili ujana wako uhuishwe kama wa tai.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Bwana hutenda haki, naye huwapa hukumu ya haki wote wanaoonewa.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Alijulisha Mose njia zake, na wana wa Israeli matendo yake.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Bwana ni mwingi wa huruma na mwenye neema; si mwepesi wa hasira, bali amejaa upendo.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Yeye hatalaumu siku zote, wala haweki hasira yake milele,
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
yeye hatutendei kulingana na dhambi zetu wala hatupatilizi kwa kadiri ya maovu yetu.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Kama vile mbingu zilivyo juu ya dunia sana, ndivyo wema wake ulivyo mwingi kwa wanaomcha;
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
kama mashariki ilivyo mbali na magharibi, ndivyo Mungu alivyoziweka dhambi zetu mbali nasi.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Kama baba alivyo na huruma kwa watoto wake, ndivyo Bwana anavyowahurumia wale wanaomcha;
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
kwa kuwa anajua tulivyoumbwa, anakumbuka kwamba sisi tu mavumbi.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Kuhusu mwanadamu, siku zake ni kama majani, anachanua kama ua la shambani;
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
upepo huvuma juu yake nalo hutoweka, mahali pake hapalikumbuki tena.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Lakini kutoka milele hata milele upendo wa Bwana uko kwa wale wamchao, nayo haki yake kwa watoto wa watoto wao:
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
kwa wale walishikao agano lake na kukumbuka kuyatii mausia yake.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Bwana ameweka imara kiti chake cha enzi mbinguni, ufalme wake unatawala juu ya vyote.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Mhimidini Bwana, enyi malaika zake, ninyi mlio mashujaa mnaozitii amri zake, ninyi mnaotii neno lake.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Mhimidini Bwana, ninyi jeshi lake lote la mbinguni, ninyi watumishi wake mnaofanya mapenzi yake.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Mhimidini Bwana, kazi zake zote kila mahali katika milki yake. Ee nafsi yangu, umhimidi Bwana.

< Zabura 103 >