< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Min Sjæl! lov Herren, og alt det, som i mig er, love hans hellige Navn.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Min Sjæl! lov Herren og glem ikke alle hans Velgerninger,
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
ham, som forlader dig alle dine Misgerninger; ham, som læger alle dine Sygdomme;
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
ham, som genløser dit Liv fra Graven; ham, som kroner dig med Miskundhed og Barmhjertighed;
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
ham, som mætter din Sjæl med det gode, at du bliver ung igen som Ørnen.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Herren øver Retfærdighed og Ret for alle fortrykte.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Han lod Mose vide sine Veje, Israels Børn sine Gerninger.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Herren er barmhjertig og naadig, langmodig og af megen Miskundhed.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Han skal ikke bestandig gaa i Rette, ej heller beholde Vrede evindelig.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
Han har ikke gjort imod os efter vore Synder og ikke betalt os efter vore Misgerninger.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
Thi saa høj Himmelen er over Jorden, har hans Miskundhed været mægtig over dem, som frygte ham.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
Saa langt som Østen er fra Vesten, har han ladet vore Overtrædelser være langt fra os.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
Ligesom en Fader forbarmer sig over Børn, saa forbarmer Herren sig over dem, som frygte ham.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Thi han kender vor Skabning, han kommer i Hu, at vi ere Støv.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
Et Menneskes Dage ere som Græs; som et Blomster paa Marken, saa blomstrer han.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
Naar et Vejr farer over det, da er det ikke mere, og dets Sted kender det ikke længere.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
Men Herrens Miskundhed er fra Evighed og indtil Evighed over dem, som frygte ham, og hans Retfærdighed med Børnebørn,
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
med dem, som holde hans Pagt, og med dem, som komme hans Befalinger i Hu for at gøre derefter.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Herren har befæstet sin Trone i Himmelen, og hans Rige behersker alt.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Lover Herren, I hans Engle! I vældige i Magt, som udrette hans Ord, idet I høre paa hans Ords Røst!
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Lover Herren, alle hans Hærskarer! I hans Tjenere, som gøre hans Villie!
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Lover Herren, I hans Gerninger alle til Hobe! i alle hans Herredømmes Steder: Min Sjæl, lov Herren!

< Zabura 103 >