< Karin Magana 8 >

1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Doth not wisdom cry aloud, And understanding put forth her voice?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
Upon the top of the high places, By the wayside, In the cross-ways, She taketh her station.
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
By the side of the gates, In the entrance of the city, In the approaches to the doors, she crieth aloud.
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
“To you, O men! do I call, And my voice is to the sons of men!
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
O ye simple ones! learn wisdom, And ye fools, be ye of an understanding heart!
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Hear, for I speak excellent things, And my lips utter that which is right.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
For my mouth speaketh truth, And wickedness is an abomination to my lips.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
All the words of my mouth are in uprightness; There is nothing crooked or deceitful in them;
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
They are all plain to the man of understanding, And right to those who find knowledge.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Receive my instruction, and not silver. And knowledge rather than choice gold!
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
For wisdom is better than pearls, And no precious things are to be compared with her.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
“I, wisdom, dwell with prudence, And find out the knowledge of sagacious counsels.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
The fear of the LORD is to hate evil; Pride, and arrogance, and the evil way, And the deceitful mouth, do I hate.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Counsel is mine, and sound reason; I am understanding; I have strength.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
By me kings reign, And princes decree justice.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
By me princes rule, And nobles, even all the judges of the earth.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
I love them that love me, And they who seek me early shall find me.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Riches and honor are with me; Yea, durable riches and prosperity.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
My fruit is better than gold, yea, than fine gold. And my revenue than choice silver.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
I walk in the way of righteousness, In the midst of the paths of equity.
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
I cause those who love me to possess substance; Yea, I fill their treasuries.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
“The LORD created me, the firstling of his course, Before his works, of old;
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
I was anointed from everlasting, From the beginning, even before the earth was made.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
When as yet there were no deeps, I was brought forth. When there were no springs, abounding with water.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Before the mountains were settled, Yea, before the hills, I was brought forth;
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
Ere yet he had made the land and the wastes, And the first of the clods of the earth.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
When he framed the heavens, I was there; When he drew a circle upon the face of the deep;
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
When he made firm the sky above, And the fountains of the deep rushed forth;
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
When he gave to the sea its bounds, that the waters should not pass their border; When he marked out the foundations of the earth, —
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
Then was I by him as a master-builder; I was his delight day by day, Exulting before him at all times;
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
Exulting in the habitable part of his earth, And my delight was with the sons of men.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
“Now, therefore, ye children, hearken to me! For happy are they who keep my ways!
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Hear instruction, and be wise! Yea, reject it not!
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Happy the man who hearkeneth to me, Who watcheth day by day at my gates, Who waiteth at the posts of my doors;
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
For he that findeth me findeth life, And obtaineth favor from the LORD;
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
But he who misseth me doeth violence to himself; All they who hate me love death.”

< Karin Magana 8 >